Jami'ar Maiduguri ta caccaki sojin Najeriya

Shugaban Jami’ar Maiduguri da ke jihar Borno ta Najeriya, Abubakar Njodi ya caccaki rundunar sojin kasar bisa ikirarinta na ceto ma’aikatan hakar man fetir da mayakan Boko Haram suka yi wa kwanton- bauna.
Njodi ya ce, har yanzu ya gaza fahimtar dalilin da ke sa rundunar sojin Najeriya ke yada labaran jabu.
Wannan na zuwa ne bayan rundunar sojin ta ce, ta ceto dukkanin manazarta kimiyyar kasa na jami’ar Maiduguri da ke aiki da kamfanin mai na NNPC.

A cewar Njodi, jami’ar ta Maiduguri ta yi rashin zaratan malamai hudu a sashen kimiyyar kasa sakamakon farmakin na Boko Haram, kuma ya ce, babu wanda ya yi kasa da shekara 10 a cikinsu yana karantawar, abin da ya bayyana da babbar asara ga jami’ar.

"Mawuyaci ne a gare ni na samu wadanda za su maye guraben wadannan malamai da muka yi rashinsu." in ji shugaban Jami'ar.

Njodi ya bayyana cewa, gano gawarwakin da sojin suka yi, ba ya nufin ceto manazartan.

Boko Haram ta dirar wa tawagar masana kimiyar kasar ne da wasu jami’an tsaro akan hanyarsu ta zuwa aikin gano man fetir a karkashin jagorancin kamfanin NNPC a yankin tafkin chadi.

Wasu rahotanni na cewa, kimanin mutane 40 ne suka mutu da suka hada da jami'an tsaro a dalilin farmakin.




Ku biyo mu a
https://www.facebook.com/isyakuweb
Don samun labaranmu ta Whatsapp ka rubuto YES a Whatsapp zuwa 08062543120 zamu aiko maka da Labaran mu kai tsaye.
Don aiko Labari ko korafi ka tuntube mu a 08062543120.
Shiga www.isyaku.com Don samun cikakken shafinmu da ke dauke da ababe masu kayatarwa.

Daga RFI

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN