Rundunar sojin sama ta Najeriya ta musanta hannu a zargi juyin mulki | isyaku.com

Rundunar sojin sama ta Najeriya NAF ta musanta zargin cewa wasu jami'anta suna da hannu a cikin zargin yunkurin juyin mulki a makonnin baya.

Daraktan labarai da hulda da jama'a na rundunar ta kasa  Air Commodore Olatokunbo Adesanya ya shaida  wa manema labarai cewa "zai kasance da mamaki a wannan karni na 21 a sami wadanda zasu yi tunanin kafewa a tsari irin na juyin mulki na soja matsawar yana cikin hayyacin tunani  na gari"

Olatokumbo ya kara da cewa rundunar sojin sama runduna ce ta kwararrun mutane masu hazaka da ilimin zamani wajen tafiyar da aikin su,kuma rundunar ta dage ne don ganin ta cimma nassara ta fannin tsare darajar Najeriya daga kowace irin barazana.



@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb Kana sha'awar ka aiko mana rahotu ? ka tuntube mu a birninkebbi080@gmail.com

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN