Gwamnatin tarayya ta gargadi masu yin kalaman tashin hankali | isyaku.com

Mukaddashin shugaban kasa Yemi Osinbajo, ya ce gwamnatin tarayya za ta hukunta duk wani mutum ko kungiya dake yin wasu abubuwa da ka iya haddasa tashin-tashina a tsakanin al’umma.

Osinbajo, ya yi gargadin ne a lokacin da yake ganawa da wasu shugabannin arewacin Najeriya a fadar shugaban kasa dake Abuja.

Wannan ya biyo bayan kira da wata kungiyar matasan arewacin Najeriya ta yin a cewa dukkanin ‘yan Kabilar Igbo su, bar yankin Arewa kafin ranar 1 ga watan Oktoba.

Ya ce ya zama wajibi gwamatin tarayya ta rika maida hankali akan duk wasu kananan abubuwa da suka taso kamar haka, dan idan an san farkon abu, ba a san karshensa ba.

Osinbajo, ya kara da cewa gwamnatin tarayya ba zata lamunci duk wani abu da ka iya barazana ga zaman lafiya a Najeriya ba, domin burin gwamnatin tarayya shine a samu zaman lafiya mai dorewa.




@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb Kana sha'awar ka sami labaranmu ta Whatsapp ? ka rubuto YES a SMS zuwa 08062543120 zamu aiko maka da Labaran mu kai tsaye kyauta a koda yaushe muka wallafa Labari.

Daga shafin Liberty

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN