Mukaddashin shugaban kasa Yemi Osinbajo, ya ce gwamnatin tarayya za
ta hukunta duk wani mutum ko kungiya dake yin wasu abubuwa da ka iya
haddasa tashin-tashina a tsakanin al’umma.
Osinbajo, ya yi gargadin ne a lokacin da yake ganawa da wasu shugabannin arewacin Najeriya a fadar shugaban kasa dake Abuja.
Wannan ya biyo bayan kira da wata kungiyar matasan arewacin Najeriya ta yin a cewa dukkanin ‘yan Kabilar Igbo su, bar yankin Arewa kafin ranar 1 ga watan Oktoba.
Ya ce ya zama wajibi gwamatin tarayya ta rika maida hankali akan duk wasu kananan abubuwa da suka taso kamar haka, dan idan an san farkon abu, ba a san karshensa ba.
Osinbajo, ya kara da cewa gwamnatin tarayya ba zata lamunci duk wani abu da ka iya barazana ga zaman lafiya a Najeriya ba, domin burin gwamnatin tarayya shine a samu zaman lafiya mai dorewa.
@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb Kana sha'awar ka sami labaranmu ta Whatsapp ? ka rubuto YES a SMS zuwa 08062543120 zamu aiko maka da Labaran mu kai tsaye kyauta a koda yaushe muka wallafa Labari.
Daga shafin Liberty
Osinbajo, ya yi gargadin ne a lokacin da yake ganawa da wasu shugabannin arewacin Najeriya a fadar shugaban kasa dake Abuja.
Wannan ya biyo bayan kira da wata kungiyar matasan arewacin Najeriya ta yin a cewa dukkanin ‘yan Kabilar Igbo su, bar yankin Arewa kafin ranar 1 ga watan Oktoba.
Ya ce ya zama wajibi gwamatin tarayya ta rika maida hankali akan duk wasu kananan abubuwa da suka taso kamar haka, dan idan an san farkon abu, ba a san karshensa ba.
Osinbajo, ya kara da cewa gwamnatin tarayya ba zata lamunci duk wani abu da ka iya barazana ga zaman lafiya a Najeriya ba, domin burin gwamnatin tarayya shine a samu zaman lafiya mai dorewa.
@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb Kana sha'awar ka sami labaranmu ta Whatsapp ? ka rubuto YES a SMS zuwa 08062543120 zamu aiko maka da Labaran mu kai tsaye kyauta a koda yaushe muka wallafa Labari.
Daga shafin Liberty
Tags:
LABARI