Ganduje yayi sulhu tsakanin Abdulmumin da Majalisar Wakilai | isyaku.com

Gwamnan jihar Kano Abdullahi Ganduje yana wani yunkuri na sasantawa tsakanin dan Majalisan Wakilai na Najeriya da aka dakatar Abdulmumin Jibrin da kakakin Majalisar Wakilai Yakubu Dogara da wasu masu mukamai a Majalisar.

Bayanai sun nuna cewa Ganduje ya riga ya tattauna da Yakubu Dogara da wadanda zancen ya shafa kuma akwai yiwuwar za'a dage kangi da aka sanya wa Abdulmumin akan ladabtarwa.

Majalisar Wakilai ta dakatar da Abdulmumin ne har tsawon kwanaki 180 na zaman  Majalisa bayan ya fallasa wata badakala a cikin kasafin kudi a Majalisar.




@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb Kana sha'awar ka aiko mana rahotu ? ka tuntube mu a birninkebbi080@gmail.com


Hoto: Leadership

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN