Ba zan lamunci rarrabuwar kai a gwamnatin Najeriya ba - Buhari | isyaku.com

Rahotanni sun ce shugaban Najeriya Muhd Buhari, yayi watsi da yunkurin wasu mukarraban gwamnatinsa, na ganin cewa ya sanya musu hannu kan wasu muhimman takardu ba ta hanyar tsallake mukaddashin shugaba, kuma mataimakinsa Farfesa Yemi Osinbajo.
Jaridar The Nation da ake wallafa ta a Najeriya, ta rawaito cewa, shugaba Buhari yaki bai wa mukarraban da suka tafi zuwa birnin London damar ganinsa, inda ya umarci da su mai dawa mukaddashin shugaban kasa farfesa Osinbajo muhimman takardun ya sa musu hannu a kai kamar yadda doka ta tanadar.

A cewar Buhari, ba zai lamunci duk wani yunkuri ba na haddasa rarrabuwar kai a gwamnatinsa.
Sai dai jaridar ta The Nation, ta rawaito cewar shugaba Buharin ya gana da mai dakinsa Aisha, a lokacin da ta kai masa ziyara a makon da ya gabata, ba kamar yadda wasu ke yadawa a shafukan dandalin sada zumunta be cewa, uwargidan shugaban kasar bata samu damar ganawa da maigidan nata ba.




@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb Kana sha'awar ka sami labaranmu ta Whatsapp ? ka rubuto YES a SMS zuwa 08062543120 zamu aiko maka da Labaran mu kai tsaye kyauta a koda yaushe muka wallafa Labari.


Daga shafin RFI

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN