Rahotanni sun ce shugaban Najeriya Muhd Buhari,
yayi watsi da yunkurin wasu mukarraban gwamnatinsa, na ganin cewa ya
sanya musu hannu kan wasu muhimman takardu ba ta hanyar tsallake
mukaddashin shugaba, kuma mataimakinsa Farfesa Yemi Osinbajo.
Jaridar The Nation
da ake wallafa ta a Najeriya, ta rawaito cewa, shugaba Buhari yaki bai
wa mukarraban da suka tafi zuwa birnin London damar ganinsa, inda ya
umarci da su mai dawa mukaddashin shugaban kasa farfesa Osinbajo
muhimman takardun ya sa musu hannu a kai kamar yadda doka ta tanadar.
A cewar Buhari, ba zai lamunci duk wani yunkuri ba na haddasa rarrabuwar kai a gwamnatinsa.
Sai dai jaridar ta The Nation, ta rawaito cewar shugaba Buharin ya gana da mai dakinsa Aisha, a lokacin da ta kai masa ziyara a makon da ya gabata, ba kamar yadda wasu ke yadawa a shafukan dandalin sada zumunta be cewa, uwargidan shugaban kasar bata samu damar ganawa da maigidan nata ba.
A cewar Buhari, ba zai lamunci duk wani yunkuri ba na haddasa rarrabuwar kai a gwamnatinsa.
Sai dai jaridar ta The Nation, ta rawaito cewar shugaba Buharin ya gana da mai dakinsa Aisha, a lokacin da ta kai masa ziyara a makon da ya gabata, ba kamar yadda wasu ke yadawa a shafukan dandalin sada zumunta be cewa, uwargidan shugaban kasar bata samu damar ganawa da maigidan nata ba.
@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb Kana sha'awar ka sami labaranmu ta Whatsapp ? ka rubuto YES a SMS zuwa 08062543120 zamu aiko maka da Labaran mu kai tsaye kyauta a koda yaushe muka wallafa Labari.
Daga shafin RFI
Tags:
LABARI