Yunkurin juyin mulki: Sojin Najeriya sun yi raddi | isyaku.com

Rundunar Sojin Nijeriya ta musanta rade-radin yunkurin juyin mulkin da wasu ke cewa an yi, inda ta ce sojojin Nijeriya ba su da niyar yi wa mulkin Dimokaradiya karan-tsaye.

A wani taron manema labarai, Kakakin rundunar sojin Nijeriya Burgediya Janar Sani Usman Kukasheka, ya ce sojojin Nijeriya masu biyayya ne ga dokokin kasa da su ka shimfida mulkin dimokaradiya.

Ya ce Sojojin Nijeriya sun ta’allaka ne ga yin biyayya ga shugaban kasa, da kuma kwamandan sojoji da tsarin mulkin kasa.

Rundunar dai, ta bukaci ‘yan Nijeriya su kwantar da hankalin su, domin babu batun karbar mulki ta hanyar karfi.

Janar Kuka-sheka, ya ce ana gudanar da bincike a kan yadda wasu rahotanni su ka ce ana zawarcin wasu sojoji domin juyin mulkin.


@isyakuweb  https://web.facebook.com/isyakuweb


Wannan labarin ya fara bayyana a shafin Liberty.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN