Rundunar Sojin Nijeriya ta musanta rade-radin yunkurin juyin mulkin
da wasu ke cewa an yi, inda ta ce sojojin Nijeriya ba su da niyar yi wa
mulkin Dimokaradiya karan-tsaye.
A wani taron manema labarai, Kakakin rundunar sojin Nijeriya Burgediya Janar Sani Usman Kukasheka, ya ce sojojin Nijeriya masu biyayya ne ga dokokin kasa da su ka shimfida mulkin dimokaradiya.
Ya ce Sojojin Nijeriya sun ta’allaka ne ga yin biyayya ga shugaban kasa, da kuma kwamandan sojoji da tsarin mulkin kasa.
Rundunar dai, ta bukaci ‘yan Nijeriya su kwantar da hankalin su, domin babu batun karbar mulki ta hanyar karfi.
Janar Kuka-sheka, ya ce ana gudanar da bincike a kan yadda wasu rahotanni su ka ce ana zawarcin wasu sojoji domin juyin mulkin.
@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb
Wannan labarin ya fara bayyana a shafin Liberty.
A wani taron manema labarai, Kakakin rundunar sojin Nijeriya Burgediya Janar Sani Usman Kukasheka, ya ce sojojin Nijeriya masu biyayya ne ga dokokin kasa da su ka shimfida mulkin dimokaradiya.
Ya ce Sojojin Nijeriya sun ta’allaka ne ga yin biyayya ga shugaban kasa, da kuma kwamandan sojoji da tsarin mulkin kasa.
Rundunar dai, ta bukaci ‘yan Nijeriya su kwantar da hankalin su, domin babu batun karbar mulki ta hanyar karfi.
Janar Kuka-sheka, ya ce ana gudanar da bincike a kan yadda wasu rahotanni su ka ce ana zawarcin wasu sojoji domin juyin mulkin.
@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb
Wannan labarin ya fara bayyana a shafin Liberty.
Tags:
LABARI