HUDUBAR JUMU'A, MAl TAKEN "YA KAI
GAFALALLEN MUTUM" DA AKA GABATAR A BABBAN MASALLACIN JIHAR KEBBI,
BIRNIN-KEBBI
4-11-2016 4—Safar-1438
Yabo ya tabbata ga Allah da Ya halicci mutum, Ya
shiryar da shi zuwa ga Alheri, Ya gargade shi daga sharri, kuma saboda haka ne
Ya aiko Manzanni, Ya saukar da littafai. Sai Ya yi bushara, Ya yi gargadi, don
a saka wa kowane rai da abin da ya aikata, Allah Marinjayi ne Mai hikima. Allah
Shi yi salatida sallama ga Manzonsa da ya zo domin ya fitar da mutane daga duhu
zuwa ga hãske da iznin Ubangijinsa Marinjayi Abin Yabo.
Bayan haka, Ya kai mutum me ke rudin ka daga
Ubangijinka Mai girma, wannan da Ya halicce ka, Ya daidaita ka, Ya kirntsa ka.
A cikin kowace siffa Ya so Ya gina ka a kanta, sai ya gina ka. Saboda me kake
shagaltuwa daga Ubangijinka sosai? Ka ce dai ba ka ji labarin Manzannin Allah
ba, ka ce an bar ka sagaga don ka yl abin da ka ga dama. Hakika ka isa wawa
rudadde. Har zuwa yaushe za ka farka ka
yi riko da shiriya? Ko sal mutuwa ta zo maka ka yi nadama lokacih da nadamarka
ba- ta da amfani?. Ya kai mutum saboda me kake rayuwa kamar wanda ba ya da Mahalicci
Mai iko a kansa? Kana rayuwa jahili gafalalle, alhali Allah Madaukaki na cewa:
"Ko mutum na jin cewa a bar shi sagaga?" Kiyama 36.Hakika ka zo Duniya
saboda babbar manufa, ita ce bautar Allah da ke cewa: "Ban halicci Aljani
da Mutum ba sai don su bauta mini" Ya kuma ce:-
Wannan da Ya halicci
rayuwa da mutuwa don ya jaraba ku (Ya ga) waye a cikin ku ya fi kyawon aiki. Mulku
2. Kuma ka zo Duniya domin ka dauki amanar da Allah ya aza wa bayin Sa, don
gyaran rayuwa da gina ta gini kyakkyawa, don samar da al’umma mai bautar Allah,
da ba ta hada wani abu da shi, ta kuma samar da jagoranci shiryaye da ke jagora zuwa ga rabbantar Duniya
da lahira. Game da wadannan mutane Allah Madaukaki ke cewa:- "Wadanda in
muka ba su iko a cikin kasa, suna tsayar da Sallah, su bada Zakka, su yi umurni
da
kyakkyawa aiki su yi hani daga mummuna”
Hajji 41 Ya kuma ce "Wadannan da ba su nunin daukakaa cikin kasa ko
barna kuma karshen kwarai na masu tsoron Allah ne". Kasasu 83.
Sai day a kai kana almubazzaranci da rayuwarka, ta
hanyar dora ta a kan jahilci da gafala da sabo, kila kowane in, kana bata
makomarka a Duniyan nan kuma a Lahira ga azaba mai radadi. Sau da yawa kana
almubazzaranci ga kanka, sai kana saba wa Allah da sunan neman abinci da neman
jin dadi, aihali Allah Madaukaki na cewa:- "Ko mu ba ku labarin masu
hasara ga ayukka? Su ne wadanda kokahnsu ya bace a rayu war ..duniya kuma su,
suna jin suna kyautata aiki ne. Kahaf 104.
Ka manta cewa Mahaliccinka Ya halicce ka ba da
izinin ka ko shawararka ko wata isa taka ba? Haka ma da ya sanya karnutum
daidaitacce, haka ma da Ya yi ka namiji ko mace. Kuma ba da shawarar ka ko roko
daga gare ka ko wata isa taka ba, Ya sanya maka ji, gani, zuciya da hankali.
Zamu ci gaba a kashi na 2.Mun rarraba hudubar saboda tsawon sa.
Kana sha'awar ka taimaka mana da labarai daga garin da kake domin mu wallafa a ISYAKU.COM? Ka tuntube mu a birninkebbi080@gmail.com ko ka aiko sakon SMS kawai zuwa 08062543120
Kana sha'awar ka taimaka mana da labarai daga garin da kake domin mu wallafa a ISYAKU.COM? Ka tuntube mu a birninkebbi080@gmail.com ko ka aiko sakon SMS kawai zuwa 08062543120
Tags:
FADAKARWA