Sojoji da 'Yan sanda sun tafka fada a Calabar | isyaku.com

Rahotanni daga birnin Calabar na jihar Cross River na cewa an tafka wani fada tsakanin 'yan sanda da sojojin ruwan Najeriya, inda ake tunanun an yi asarar rayuka da wasu da dama kuma sun jikkata.

Rundunar 'yan sandan Najeriya ta tabbatar da  faruwar lamarin, inda har ta wallafa hotunan barnar da ta ce sojojin sun yi a ofishin 'yan sandan.

Amma rundunar ba ta yi karin bayani kan asarar rayuka ko jikkata ba.

Wasu rahotanni sun ce rikicin ya fara ne a yayin da wani dan sanda ya yi kokarin tsayar da motar sojojin, wadda ta ki bin umarnin danjar bayar da hannu.

Fadan ya yi kamari ne yayin da wasu manyan jami'ai suka yi kokarin sasantawa, amma daga bisani sai al'amura suka rincabe.

Kafar yada labarai ta Premium Times ta ruwaito cewa wani ganau ya shaida mata cewa daga nan sai sojojin suka shiga cikin ofishin 'yan sandan na Akim inda suka fara harbe-harbe suka kuma kona ofishin.




@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb Kana sha'awar ka aiko mana rahotu ? ka tuntube mu a birninkebbi080@gmail.com



Wannan labarin ya fara bayyana a shafin BBC

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN