Rundunar Vigilante ta jihar Kebbi: A shirye muke mu kara inganta tsaro a jihar Kebbi | isyaku.com




Kwamandan rundunar sa kai na tsaro da aka fi sani da suna Vigilante group of Nigeria reshen jihar Kebbi Kwamanda Muhammed Lawal Augie wanda bangaren su ne Gwamnatin jihar Kebbi ta tabbatar da sahihancin su ya yi bayani akan matsalolin da rundunar shi ta Vigilante take fuskanta a wani tattaunawa da ISYAKU.COM yayi da shi a hedikwatar rundunar da ke fuskantar babban kasuwar Birnin kebbi.



Kwamanda Lawal Augie ya shaida mana cewa zamani ya canza hakama marasa gaskiya basa tafiya hannu sake suna tafiya da bindigogi irin na zamani amma duk da haka 'yan Vigilante suna tare da Allah kuma kundin tsarin aikin su ya yarda da su dauki bindigogi kirar gargajiya,saboda haka ya kamata Gwamnati ta taimaka ma rundunar domin a sami wadatattun irin wadannan bindigogin ga jami’an rundunarsa a fadin jihar Kebbi.Kowace karamar hukuma ta mallaki nata kana Hedikwata ya zama tana da nata don tukarar kalubalen tsaro.



Augie ya kara da cewa a horo da suka samu daga rundunar sojan Najeriya da hukumar ‘yan sanda ta Najeriya jami’i zai iya zama da bindiga da harsasai har ya shiga aikin tsaro yayi ritaya bai harba ko kwara daya ba domin harbi yana tafiya ne tare da doka da oda,illa ana rike bindigar ne domin kariya ba wai mutum yayi amfani das hi ba a bisa lissafin kansa."Rashin wadannan makaman yana daya daga cikin matsalolin mu,idan aka bamu bindigogin a bisa horarwa da muka samu bazamu je mu harbi wadanda bai kamata ba".



Bincike da ISYAKU.COM ya yi ya nuna cewa ofishin Vigilante na jiha baya da kaso na kowane wata a zaman tallafi ga rundunar daga Gwamnatin jiha,amma ofishin kan sami tallafi idan da wani bukata na tsaro da ake bukatar Vigilante domin su taimaka wa sauran jami’an tsaro wajen bayar da kariya ko tsaro.



Kwamanda Lawal Augie ya roki Gwamnatin jihar Kebbi akan ta kara taimaka ma rundunarsa da motoci koda lalatattu ne wadanda aka karba daga ‘yan sanda sai a gyara a basu su zasu hakura dasu wajen tafiyar da aikin su.Kwamandan ya kuma bada misalin wani barawo da suka kama wanda ya shahara wajen satan injimin ban ruwa na noman rani bayan bayani da suka yi da shi ya nuna cewa ya saci injin 18 a garin Argungu,amma da suka tsananta bincike ala tilas sauran injin 17 suka fito bayan 18 na farko,ya kara da cewa wannan ai zagon kasa ne ga shirin Gwamnati na inganta aikin noma musamman noman rani.



Kwamandan ya shaida mana cewa rundunasa tana da mutum 8000 a fadin jihar Kebbi,amma mutum 1400 ne ‘yan sanda suka horar da su,yayin da mutum 1060 kuma Sojoji ne suka horar da su "bayan mun sami horon mukan dawo mu horar da jami’an mu abin da muka koya".Kwamadan ya kara rokon Gwamnati akan ta taimaka ma rundunarsa da na’urorin sadarwa domin saukaka tafiyar da aiki ta hanyar sama masu radiyon ova-ova da sauransu.



Yayin da ISYAKU.COM ya tuntube shi akan zargi da wasu ke yi wa jami’ansa akan cewa sukan yi abin da wasu ke ganin cewa shiga sharo ba shanu ne akan wasu lamura da ba hurumin rundunar Vigilante ba sai Kwamanda Lawal Augie ya shaida mana cewa ba shiga sharo ba shanu bane,yace doka ta ba rundunarsa dama tayi sulhu a dukkan lamurra da zai kai ga samun zaman lafiya a cikin al’umma da kasa baki daya.Ya shaida mana cewa ai kara da da ake kawowa jama’a ne ke kawowa ba wai Vigilante ne ke yin awon gaban kanta ba.


@isyakuweb  https://web.facebook.com/isyakuweb

 
Kana sha'awar ka taimaka mana da labarai daga garin da kake domin mu wallafa a ISYAKU.COM? Ka tuntube mu a birninkebbi080@gmail.com ko ka aiko sakon SMS kawai zuwa 08062543120




Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN