Mukaddashin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo, ya yi ganawar sirri
da tsohon mataimakin shugaban kasa Namadi Sambo a fadar shugaban kasa da
ke Abuja.
Yayin da ya ke zantawa da manema labarai jim kadan bayan ganawar, Namadi Sambo ya ce ya kai Osinbajo ziyarar sada zumunta ne kawai ba wani al’amari na daban ba.
Ya ce ziyara makamanciyar wannan ba sabon abu ba ne, kamar dai yadda tsohon ubangidan sa Goodluck Jonathan ya sha kai wa shugaba Buhari ziyara a ofishin sa da ke Abuja.
Wannan dai ita ce ziyara ta biyu da Namadi Sambo ya kai mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo, tun bayan da aka rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayu na shekara ta 2015.
@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb
Wannan labarin ya fara bayyana a shafin Liberty tvradio
Yayin da ya ke zantawa da manema labarai jim kadan bayan ganawar, Namadi Sambo ya ce ya kai Osinbajo ziyarar sada zumunta ne kawai ba wani al’amari na daban ba.
Ya ce ziyara makamanciyar wannan ba sabon abu ba ne, kamar dai yadda tsohon ubangidan sa Goodluck Jonathan ya sha kai wa shugaba Buhari ziyara a ofishin sa da ke Abuja.
Wannan dai ita ce ziyara ta biyu da Namadi Sambo ya kai mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo, tun bayan da aka rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayu na shekara ta 2015.
@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb
Wannan labarin ya fara bayyana a shafin Liberty tvradio
Tags:
LABARI