Rahotanni daga fadar shugaban
Najeriya Muhammadu Buhari ana cewa shugaban bai fito taron majalisar
ministoci da aka saba yi duk ranar Laraba ba, wanda hakan ya zama karo
na uku kenan a jere da bai halarta ba.
Ya ce, mataimakin shugaban Farfesa Yemi Osinbajo ne ya jagoranci taro wanda aka fara da misalin karfe 11 na safiyar Larabar
Dama dai ana ta rade-radin cewa lafiyar shugaba Buharin na cikin wani yanayi mara dadi, duk da cewa a ranar Talata an bayar da rahoton fitowar sa ofishinsa na cikin gida, inda har ya gana da wasu manyan jami'an gwamnatin kasar biyu.
An yi wannan taro an gama ne tsakanin mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo da ministocin kasar.
Tun farkon fara taron shugaban bai bayyana ba kuma ba alamu na bayyanarsa, ba kamar karon farko da bai zo taron ba inda aka yi ta jiran zuwansa kafin daga bisani aka ce Mista Osinbajo ya ja ragamar taron.
A wannan karon kai tsaye aka fara taron da isar Mista Osinbajon.
Da yake kafofin yada labarai sun wallafa labarin rashin halartar shugaban tun kafin kammala taron, hakan tasa da fitowar su, ministan yada labarai na kasar Alhaji Lai Mohammed ya shaidawa manema labarai dalilin rashin halartar shugaban a wannan karo.
Mista Mohammed ya ce, shugaba Buharin bai fito ba ne saboda har yanzu yana bin shawarwarin da likitoci suka ba shi cewa ya ci gaba da hutawa a gida.
Lai ya ce rashin lafiyar shugaban ba ta kai yadda ake kururutawa a shafukan sada zumunta da muhawara ba.
An dai ci gaba da ce-ce-ku-ce a kasra kan halin da lafiyar shugaba Buharin ke ciki.
@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb
Me ya sa Buhari bai halarci taron majalisar ministoci ba? ya fara bayyana ne a shafin BBC Hausa
Tags:
LABARI