Kebbi: Gwamnati ta bayar da tallafin Naira Miliyan 3 ga wadanda suka rasa muhalli a Ribah

Mataimakin Gwamnan jihar Kebbi Alh.Samaila Dabai Yombe ya bayar da tallafin naira miliyan 3 wa wadanda suka rasa muhallin su sakamakon ruwan sama da aka yi a garin Ribah a karamar hukumar Danko/Wasagu da ke Masarautar Zuru.

Mataimakin Gwamnan ya baiwa wata mata da mijinta ya rasu Naira Miliyan daya bayan gidan da take ciki ya salwanta yayin da sauran wadanda abin ya shafa aka basu Naira Miliyan biyu,

Samaila Dabai Yombe ya umarci Kantoman karamar hukumar Danko/wasagu akan ya tsara sunayen wadanda lamarin ya shafa domin Gwamnati ta tsara yadda za'a taimaka masu,haka ma hukumar bayar da agaji na gaggawa ta Najeriya NEMA .


@isyakuweb  https://web.facebook.com/isyakuweb

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN