Bincike ya nuna cewa kashi 57 na 'yan Najeriya sun amince da Gwamnatin APC | isyaku.com

Wani rahoto da cibiyar tabbatar da kafuwar dimokradiyya a Nijeriya ta  fitar, ya nuna cewa kashi 57 cikin 100 na ‘yan Nijeriya sun gamsu da gwamnatin shugaban Muhammadu Buhari.

Cibiyar, da sauran kungiyoyin kare muradun gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari ne su ka fitar da wannan rahoto.

Rahoton ya ce,  kashi 57 cikin 100 da ke wakiltar mutane 4,097 a kananan hukumomi 111 da ke Nijeriya, sun yarda da cewa gwamnatin shugaba Buhari ta yi rawar gani a cikin shekaru biyu.

A bangaren  yaki da cin hanci da rashawa kuwa, kashi 52 cikin 100 sun amince da matakan da gwamnati ke dauka, amma kashi 47 cikin 100 ba su amince da matakan ba.



@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb Kana sha'awar ka aiko mana rahotu ? ka tuntube mu a birninkebbi080@gmail.com


Wannan labarin ya fara bayyana ashafi Liberty.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN