An kashe mutane 8 a hari kan makarantar Islamiyya a Afganistan

Mutane 8 ne suka mutu sakamakon harin bam da aka kai kan wata makarantar Islamiyya a jihar Pervan ta kasar Afganistan.
Shugaban 'yan sandan Pervan Muhammad Zaman Mamuzay ya bayyana cewa, an saka bam din a karkashin kujerar da shugaban Shura na malaman Pervan Mevlevi abdul Rahim Hanafi ya ke zaune a kai.
Mamuzay ya ce, bam din ya fashe a lokacin da ake tsaka ba wa daliban Hanafiyya karatu.
Ya ce, daliban Hanafiyya 7 ne suka mutu inda wasu 6 suka jikkata sakamakon harin.
Shugaban 'yan sandan ya ce, kungiyar ta'adda ta Taliban ce ta kai harin.
Har yanzu babu wani da ya dauki alhakin kai harin.

@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb

 An kashe mutane 8 a hari kan makarantar Islamiyya a Afganistan ya fara bayyana a TRT

 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN