Uwar yara 8 ta mutu bayan ta zubar da juna biyu da saurayin ta yayi mata

Wata mata uwar yara takwas ta mutu a jihar Ogun a yayin da ta zubar da juna biyu da saurayin ta ya yi mata, matar mai suna Sukurat Adedoyin bayanain sun nuna cewa tana da aure ko kafin aukuwar wannan mummunar lamarin.

Jaridar Sunday Vanguard ta wallafa cewa matar 'yar shekara 33 ta sami kanta cikin wannan yanayi ne bayan saurayin ta mai suna Alabi Kamilu ya banka mata ciki kuma ya bukaci dole ta zubar da cikin inda ita mariganyar ta nemi taimakon wata ma'aikaciyar jinya mai suna Abosede Bello wadda ita ta tafiyar da aikin cire cikin kuma aka sami akasi daga bisani.

Jami'in dan sanda mai gudanar da bincike Asake Morowuntonu ya ce Kamilu saurayin mariganya Sukurat shi ne ya tilasta a dole a cire jikin.


@isyakuweb  https://web.facebook.com/isyakuweb

Hoto: Globalhealth

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN