Putin ya gargadi Trump: Amurka zata fuskanci hakikanin yaki idan ta sake kai wa Syria hari

Bisa dukkan alamu shugaban Rasha Vladmir Putin da Donald Trump na kasar Amurka dangantaka yayi tsami kuma ya kai ga tayar da jijiyoyin wuya bayan harin da Amurka ta kai wa  kasar Syria wadda Rasha ke kawance da ita kuma take goya mata baya.

Shugaban Rasha Vladmir Putin ya gargadi Amurka akan cewa matsawar ta sake kai hari a kan kasar Syria,lallai ta shirya fuskantar hakikanin yaki.

Amurka tayi awon gaban kanta ne inda ta kai hari da makamai masu linzami akan rundunar sojin Kasar Syria a bisa zargin cewa kasar Syria ta kai harin rashin imani da iskan gas mai lahani akan yankin da 'yan tawaye ke rike da shi a kasar Syria.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN