Mutane 20 sun mutu a zanga-zangar Venezuela

Alkaluman mutanen da suka gamu da ajalinsu a wata zanga-zangar adawa da gwamnatin Venezuela sun kai 20 bayan wata sabuwar arangama ta barke tsakanin jami’an tsaro da masu zanga-zangara a birnin Caracas.
Jami’an ‘yan sandan kwantar da tarzoma sun yi ta harba hayaki mai sa kwalla, in da kuma wasu zaune gari banza suka yi ta harba bindiga kan gidajen al’umma kamar yadda kamfanin Dillancin Labarana Faransa na AFP ya rawaito.
Sai dai wasu rahotanni na cewa, mutane 8 sun rasu ne sakamakon fadowar wayar wutar lantarki kan masu zanga-zangar ganin shugaba Nicolas Maduro ya sauka daga kujersa.
'Yan adawa na zargin gwamnati da hayo 'yan daba don kai musu farmaki a yayin zanga-zangar.

@isyakuweb ku biyo mu a Facebook

Mutane 20 sun mutu a zanga-zangar Venezuela ya fara bayyana a RFI






 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN