Mai
Martaba Sarkin Zuru Maj. Gen. (Dr.) Muhammadu Sani Sami CON, Mni, LLD, FICEN,
Sami Gomo II ya fara rangadin Kasarsa. Sarkin ya fara ne da Kasar Wasagu a inda
yaziyarci Iyayen Kasa biyar dake wannan Masarauta wato Bena, Wasagu, Kanya,
Waje da Ribah.
A
kowace Fada Mai Martaba Sarkin yakan yabawa Gwamnatin Jihar Kebbi a karkashin Senata
Atiku Bagudu da kuma ta Tarayya akan irin ayyukan da sukewa Kasa. Sannan yakarbi
koken su tareda kira garesu dasu tabbatarda sun sanya ‘ya’yansu Makaranta musamman
Mata, ya kara yin kira garesu dasu dawoda tsarin tsaro irin nada inda kowane Basarake
ko Mai unguwa zai tabbatar da bakin da ake samu a Kasarsa na kirki ne ko akasin
haka tareda kai rahoton batagari a wurin hukuma.
Koken da Sarakunan wadannan wuraren sukagabatar sun hada da:
1. Kira a tallafa wa
ilimin mata a Bena ta hanyar gina Makarantar Sakandare ta jeka ka dawo ta Mata a Bena.
2. Daukar matakin magance
matsalolin iyaka tsakanin Bena da Jihar Niger da kuma Ribah da Kasar Dabai.
3. Gina Banki a
garin Ribah.
4. Gina Dam
tsakanin Ribah da Waje.
5. Kara maida Burtullai
da mashekarai da kuma mashaya a hannun Fulani don kaucewa fadan Fulani da
Manoma.
6. Kara inganta tsaro
a wannan yanki.
7. Samarwa matasa ayukan
yi a Gwamnatin Tarayya.
A
jawabinsa na godiya Mai Martaba Sarkin Wasagu Alh. Mukhtar Musa Muhammad Wasagu
ya godewa Mai Martaba akan irin kula da yakewa jama’arsa tare da tabbatar masa
wannan yanki nasa an samu tsaro da zaman lafiya. Sai abin da ba’arasa ba sannan
ya kara gode masa akan irin ayukkan da ake aiwatarwa a wannan
yanki.