Makonni uku da suka gabata,Duniya ta shaida matakai maras
takamammen alkibla da kasar Amurka ta dauka game da rikicin kasar Syria.A watan
Maris daya gabata kasar Amurka ta kai hari a unguwannin fararen hula a
Raqqa,harin da yayi sanadin lalata wata Makaranta da kuma Masallaci haka kuma
harin ya janyo mutuwar mutane da dama kuma fararen hula.Bayan mako daya,Nikkey Haley
jakadiyar kasar Amurka a Majalisar dinkin duniya ta ce, kasar Amurka bata da
bukatar cire shugaban kasar Syria Bashar Al-assad daga mulki da karfin tuwo.
Mako daya bayan jakadiya Nikkey tayi wannan jawabi, kwatsam
sai kasar ta Amurka tayi awon gaban kanta ba tare da albarkacin Majalisar
dinkin Duniya ba ta kai hari a wani filin sauka da tashi na jiragen sama wanda
jiragen yakin sojojin Rasha da na Syria
ke amfani da shi matuka domin sukai hare-hare akan tsigeru ‘yan tawaye a kasar
ta Syria.Wannan matakin a karon farko ya nuna yadda kasar Amurka ke takalan
sojojin na kasar Syria domin idan sun mayar da martini a bisa dalili na kare
kansu ita kuma kasar ta Amurka sai tayi amfani da wannan dama domin ta tsunduma
haikan ta fuskanci kasar Syria da yaki gadan-gadan.
Amurka dai karkashin jagorancin Donald Trump,ta kafa hujja
ne akan wasu hotuna da aka wallafa wanda ke nuna wasu yara da mutane a yanayi
na tagayyara akan zargin cewa anyi amfani da iskar guba ne akan mutanen.Bayan mumunar bala’I da mutanen
kasar Syria ke fuskanta a sanadin wannan yaki,Trump ya bayyana muguntar sa a
fili ,a sakamakon harin da sojojin kasar Amurka suka kai akan sojojin
Syria,’yan tawayen Syria sunyi murna da wannan lamarin kuma a yanzu haka suna
sake hadewa domin su karfafa bayan a ‘yan makonnin da suka gabata sojojin Syria
sun ci galaban su har suka tarwatse.
Wannan yana nuna ma Duniya cewa za’a sami canji kenan a irin
rawar da kasar Amurka take takawa a rikicin kasar Syria wanda zata jagoranci
wasu kawayenta domin akai yaki akan Gwamnatin Bashir Al-asad da kawayen
ta?.Idan ‘yan tawayen kasar Syria suna ganin kamar shugaba Trump zai goyi bayan
su kai tsaye domin ya taimaka masu su kawar da Gwamnatin Syria,amsa a nan shine
sunyi kuskure,domin Trump ba mutum bane da ke tausayin ‘yan kasar Syria akan
dalilin cewa babu abin day a tabuka a shekaru shida na yakin domin ya kawo
sauki a cikin lamarin.
Wani dali kuwa shine Trump ba zai so yagan cewa Amurka ta
maimata kuskuren da take ta yi ba a wannan yankin na gabas ta tsakiya,kamar
yadda Gwamnatin Reagan ta taimaka ma Ayatullah Khomeini a 1979 a juyin juwa
halin daya zama sanadin kafa kasar Shi’a mafi karfi a Duniya wanda a yanzu haka
ta zama barazana ga kasara Amurka.Haka kuma yadda George Bush ya jagoranci yaki akan Gwamnatin Iraqi ta
Saddam Hussein yakin daya zama sanadin kisan wulakanci ga shugaba Saddam Hussei
wanda hakan ya haifar da kungiyoyin ta’addanci kamar su IS wanda ta samo asali
daga cikin kasar Iraqi.Haka kuma Amuka da Faransa suka jagoranci kashe shuga
Mu’ammar Gaddafi na kasar Libya,wanda hakan ya haifar da kungiyoyin ta’addanci
da suka zama barazana ga tsaro a yankin Maghreb.
Gwamanati Trump dai bata da kwarewa akan harakokin kasashen
Duniya kuma Gwamnati ce da take tafe da rashin farin jinin ta koma bayan abin
da aka sani na tsarin kasar Amurka matukar Amurka ta kai hari to zaka gani cewa
anyi haka ne domin jinkai ko kawar da ta’addanci kamar yadda muka gani a
shugabancin Reagan,Clinton,Bush da Obama.
Awannan yanayin, dole ne akai zukata nesa musamman kasar
Rasha saboda idan Rasha tace ta mayar ma Amurka da kaidin ta,lallai Amuka zata
dandana kudarta kuwa.Domin idan Rasha ta kara bayar da taimakon makaman linzami
da rokoki masu kakkabe jiragen sama da sunfurin rokoki masu dakile hari daga
rokoki kwatan kwacin irin wanda Amurka ta harbo wa kasar Syria,lamarin ba zaiyi
kyau ba domin yakin na kasar Syria Allah ne kadai ya san lokacin da zai
kare.Mafita na siyasa kadai ne abu mafidacewa da zai kawo karshen yakin kasar
Syria.
Sharhi daga Isyaku Garba