Gwamnatin PDP tayi kokari a shekaru 16 - Jonathan

Tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan, ya ce jam’iyyar PDP ta fadi zaben shekara ta 2015, amma ba don gazawar gwamnatin ta ba.

Jonathan ya bayyana haka ne a Abuja, inda ya ce a kowace kasa ana samun haka, amma ba don gazawar jam’iyya mai mulki ba, sai domin kawai ‘yan kasa su na bukatar samun canjin shugabanni.

Tsohon shugaban kasar, ya kuma yi watsi da maganganun da gwamnatin APC ke yi cewa, jam’iyyar PDP ba ta tsinana wa Nijeriya komai a tsawon shukaru 16 da ta yi ta na mulki ba.

Jonathan ya kara da cewa, ba bakon abu ne jam’iyyar siyasa ta fuskanci matsala ba, domin a cewar sa, kowane zabe ya na iya zama darasi ga kowace jam’iyyar siyasa.

A karshe Jonathan ya ce, ya na alfahari da cewa jam’iyyar PDP ta taka gagarumar rawa wajen tafiyar da mulkin Nijeriya yadda ya kamata na tsawon shekaru 16.


Liberty
@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN