Dan kasuwa ya maka su Saraki Kotu akan tantance Magu

Wani kasurgumin dan kasuwa mazaunin Lagos Raji Rasheed Oyewumi, ya maka shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki da wasu sanatoci kotu a kan rawar da su ka taka wajen tantance Ibrahim Magu a ranar 15 ga watan Maris da ya gabata.

Dan kasuwar dai, ya bukaci kotu ta soke sakamakon da majalisar dattawan ta fitar dangane da matsayin Ibrahim Magu.

Oyewunmi ya kuma bukacin kotun ta haramta wa Bukola Saraki da wasu ‘yan majalisa 10 halartar zaman tantance Magu nan gaba, domin a cewar sa, ba za su yi ma shi adalci ba a matsayin wandanda ke fuskantar tuhume-tuhume a hukuamar yaki da cin hanci da rashawa.

‘Yan majalisar da aka yi karar kuwa sun hada da Godswill Akpabio, da Jonah Jang, da Aliyu Magatakarda Wamako, da Stella Oduah, da Theodore Orji, da Rabi’u Musa Kwankwaso, da Ahmed Sani Yeriman Bakura, da Danjuma Goje, da Josua Dariye, da kuma Adamu Abdullahi.


Liberty

@isyakuweb https://web.facebook.com/isyakuweb

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN