An kashe mutane 5 a tagwayen harin da aka kai a Maiduguri

Rahotannin daga gwamnatin Najeriya na nuna cewa mutane 5 ne suka mutu a tagwayen hari da aka kai  a Maiduguri na kasar Najeriya inda 11 kuma suka jikkata.

Kakakin Hukumar bayar agaji gaggawa ta Najeriya Abdulkadir Ibrahim ya shaidawa dan jaridar Anadolu cewa a ranar Laraban nan an kai harin kunar bakin wake 3 a Maiduguri inda mutane  5 suka mutu tare da jikkata 11.

 A gefe guda kuma mai magana da yawun Wyan sandan yankin Victor Isuku ya bayyana cewa daya daga cikin 'yan harin yayi kokarin shiga sansanin masu neman mafaka suke a kauyen Usmati.
Ya kaa da cewa, "ya kai harin ne a yayin da mutane suka yi kokarin hana shi shiga yankin."

A halin yanzu an kai wadanda suka jikkata zuwa asibiti domin jiyya.
Ko da yake babu wanda ya dauki alhakin harin amma sai dai 'yan sanda sun dora alhakin kan 'yan Boko Haram. Domin a baya ta kai irin wannan hare-haren.



TRT

@ISYAKUWEB     https://web.facebook.com/isyakuweb

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN