Zargin Fyade: Basarake yayi wa 'yar shekara 15 fyade a Katsina

Wata majiya ta shaida wa manema labarai cewa Majalisar masarautar Katsina ta dakatar da Bashir Bala Kofar-bai daga mukamin sa na Magatakarda, bisa zargin aikata laifin fyade da ake yi masa.

Tun makonni biyu da suka gabata ne Magatakardan ke fuskantar shari'ar aikata fyade ga wata yarinya 'yar shekara 15 a Katsina.Wata majiya ta labarta cewa yarinyar ta fada cikin wannan ibtil'i ne bayan mahaifinta ya aike ta gidan Magatakardan.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Sakataren Majalisar masarautar Bello Ifo, ya ce dakatarwar ta fara aiki ne nan take.


@isyakuweb--Ku biyo mu a facebook
https://web.facebook.com/isyakuweb

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN