Wani Mutum da dansa sun mutu a cikin Rijiya





Wani ibtila'i ya faru a wani kauye da ake kira garin Fulani a Karamar hukumar Wamakko kusa da Sokoto inda wani mutum mai suna Malam Umar da danshi Abubakar suka  rasa ransu a yayin da rijiyar da suke hakawa ya ruftawa Abubakar bayan an gina rijiyar har tsawon mita 9.Ganin haka ne ya sa mahaifin Abubakar shima ya tsunduma cikin rijiyar domin ya ceto dansa Abubakar,amma da yake ajali yayi kira babu wanda ya fito da rai a cikin su.


Rahotanni sun nuna cewa 'yan kwana kwana sun zo wajen da abun ya faru kuma suka fitar da gawakin guda biyu daga bisani aka yi masu sutura

@isyakuweb   Ku biyo mu a Facebook https://web.facebook.com/isyakuweb

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN