Bayan jinya na kwanaki 50 a London,Shugaba Muhammadu Buhari ya koma bakin aiki yau Litinin 13/3/2017 bayan ya rubuta takarda da ya shaida wa Majalisar Wakilai ta NASS da ke Abuja.
Wannan ya kawo karshen shugabancin riko da shugaba Buhari ya baiwa mataimakinsa Yomi Osinbanjo a yayin da ya bar Najeriya zuwa London domin jinya.Buhari dai yayi abin da Gwamnatotin da suka wuce basu yi ba na mika wa mataimakinsa cikakken ikon tafiyar da ragamar mulki har iya tsawon lokacin da yayi a lokacin da yake jinya.
Daga Isyaku Garba
@isyakuweb ku biyo mu a facebook https://web.facebook.com/isyakuweb
AIKO DA LABARI