Kimanin mutane 46 aka kashe kuma akalla mutane 100 suka jikata a mummunar rikicin kabilanci da ya faru a garin Ile-Ife da ke jihar Osun.
Hukumar 'yansandan Najeriya ta tabbatar da mutuwar mutane 46,sabanin bayanin da hukumar ta yi tun farko cewa mutum 20 ne aka kashe a rikicin.
Kusan mutane 100 suka jikkata a rikicin tsakanin Hausa da Yarabawa da ya faru a ranar 8 ga watan Maris a unguwannin Sabo da Lagere.
@isyakuweb -Ku biyo mu a Facebook
https://web.facebook.com/isyakuweb
Tags:
LABARI