Ministan albarkatun ruwa na Najeriya Engnr.Suleiman Adamu ya ziyarci jihar Kebbi kuma ya zarce zuwa wajen aikin noman rani da ke Fadama a garin Birnin kebbi In da yakai ziyar gani da ido na gyaran Zauro polder project dake fadamar Birnin kebbi.Ministan tare da tawagar sa sun zagaya cikin Fadamar inda suka gane wa idanun su irin kokari da manoman rani ke yin a noman shinkafa,alkama da sauran su.wannan wurine da ake noman rani na amfani gona iri iri a karkashin kulawar hukumar raya fadamar rima watau Sokoto Rima River Basin Development Authority Birnin kebbi
Ministan ya bayyana jin dadin sa akan yadda manoma suka
dukufa sosai wajen noman na rani,bayan ya duba aikin da ake yi a Gidan ruwa na
fadamar domin inganta samar da wadataccen ruwa ga manoma a Fadamar,Ministan ya
shawarci manoma akan su dinga aikin taimako na kai-da kai domin samun
ingantaccen sakamako a tafiyar da aikin su na noman rani.
Duk da yake Ministan ya nuna farin ciki akan abin da ya gane
wa idanun sa,amma kwanaki kadan kafin zuwan Ministan ,ISYAKU.COM ta zagaya
Fadamar inda muka gan manoma suna amfani da ingin ban ruwa mallakin kansu domin
samar da ruwa domin amfanin gona da suka shuka.Bincike ya nuna cewa har zuwa
wani lokaci ba a samar masu ruwa daga ingin na ban ruwa da yake a Gidan ruwa da
ke cikin Fadamar sakamakon matsala da ake kyautata zaton cewa injin din ya
fuskanta.
A nashi jawabi shugaban Manoma na Fadama Polder Alh.Shehu Mai Bulo wanda aka fi
sani da Alh.Shehu Dan Nagwari ya nuna jin dadin sa a kan ziyarar ta Ministan
kuma ya yaba wa Ministan akan kokari da ya ce Ministan ke yi domin inganta
harkokin albarkatun ruwa da noman rani a Fadamar.
Kalli bidiyo a kasa
Isyaku Garba
@isyakuweb KU BIYO MU A FACEBOOK
Tags:
LABARI