Magidanci yayi wa 'yan mata 2 fyade

Malam Lawal Zubairu wani dan kasuwa ne a garin Kano da ya gurfana a gaban Kotu akan zargin yi wa wasu tagwayen 'yan mata 2 masu shekara 11 fyade.Karar da aka shigar ranar 18 ga watannan ya biyo bayan kara da mahaifin 'yan matan ya kai ne wa 'yan sanda wanda sanadin hakan yakai ga gurfanar da Malam Zubairu a gaban kotu.

Rufa'i Yunusa dan sanda mai gabatar da kara yayi wa kotu jawabi yadda Lawal Zubairu ya rudi 'yan matan suka bishi zuwa gidan sa inda ya aikata wannan aika aikan.Malam Lawal dai bai amsa laifin sa ba sanadin hakan Alkali ya daga shara'ar zuwa ranar 27 ga watan Afrilu,ya kuma bada umarni cewa a ci gaba da tsare Lawal Zubairu har zuwa lokacin.

@isyakuweb--Ku biyo mu a Facebook
https://web.facebook.com/isyakuweb

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN