Labarai daga wasu kafofin Labarai na Waje

BBC

Shugaban rikon kwarya na hukumar EFCC mai yaki da yi wa tattalin arzikin Najeriya zagon kasa, Ibrahim Magu, ya ce wadanda ke tsoron kada a fallasu ne suke yakar sa.
A makon da ya gabata ne dai majalisar dattawan kasar ta ki amincewa da shi a matsayin tabbataccen shugaban hukumar ta EFCC.
Kuma wannan shi ne karo na biyu da majalisar ke kin tabbatar da shi.
'Yan majalisar dai na kafa hujja da cewa sun sami rahoto kan Magu daga hukumar tsaron farin kaya, DSS, ta kasar dake zarginsa.
Rahoton dai ya nuna Ibrahim Magu na da tabon laifi abin da ke sanya shakku kan yiwuwar yakar cin hanci da rashawa.
A wannan hirar da ya yi da Ahmed Abba Abdullahi, Ibrahim Magu ya ce ba haka al'amarin yake ba.

RFI  
 
Wata kotu a kasar Janhuriyar Nijar ta sallami wasu fararen hula 15 da ake tsare dasu bisa zargin hannu  a yunkurin kifar da Gwamnatin Shugaba Muhammadu Isufu a shekara ta 2015.
Lauyan mutanen  Ali Kadir ya tabbatar da sakin mutann da yake karewa.
A watan 12 na shekara ta 2015 ne dai Gwamnatin Muhammadu Isufu ta sanar da cewa ta yi nasarar hana juyin mulki, kuma tana tsare da wasu mutane dake da hannu a ciki.
Majiyoyin samun labarai na cewa an sallami mutane 15, amma kuma akwai manyan sojoji 9 da suka hada da jagoran kifar da Gwamnatin Janar Salou Souleymane wadanda har yanzu ake tsare dasu.

DW
Sama da watanni uku ke'nan kungiyar Boko Haram ke zafafa kai hare-haren kunar bakin kusan kowane mako a wuraren taron jama'a musamman masallatai ko kuma sansanonin 'yan gudun hijira a Maiduguri, inda ake samun hasarar rayuka da dukiyoyi da dama. Haka a iya cewa kusan kullum sai jami'an tsaron ko kuma matasa masu ayyukan sa kai na CJFT sun dakile hare-haren kunar bakin wake cikin dare ko da sanyin asubahi wanda yawanci aka fi amfani da mata masu kanan shekaru.
Yachilla Bukar ta Radio Dandak Kura tare da 'yan gudun hijira
Kungoyin mata sun bayyana damuwa kan yadda ake amfani da mata wasu kanan shekaru wajen kai hare-haren kunar bakin wake a wannan lokaci. Hajiya Ya Gana Alkali ita ce shugabar gamayyar kungiyoyin mata ta Najeriya reshen jihar Borno ta bayyana yadda suke ji da wannan hali da ake fama da shi a Maiduguri a matsayin wani babban kalubale da ya kamata kowa ya bada nashi taimako dan ganin masu wannan akidar basu samu nasara ba.
Karuwar harin kunar baki wake a birnin Maiduguri dai ya sa al'ummar yin tambayar makasudin dawowar hare-haren bama-baman. gwamnan Jihar Borno kashim Shetima a wata tattaunawa da muka yi da shi ya bayyana cewa abin da ya ke faruwa abin bakin ciki ne kuma gwamnati na daukar matakai don magance matsalar.

Sojojin Najeriya a bakin aiki na tsaro a Maiduguri
Sai dai duk da irin wadan nan hare-hare da ake kaiwa harkoki na yau da kullum na ci gaba da gudana, inda mutane ke zuwa kasuwanni da wuraren ibada ba tare da zullumi ko fargabar wani abu zai same su ba. A wurare kamar Post Office da Custom da kuma bakin kasuwar Monday Market za a lura cewa mutane suna sha'anin kasuwancinsu cikin cinkuso kuma babu wasu matakai na tsaro da a zahiri za'a ce an sa don magance irin hare-haren da ake kaiwa.
 

VOA
 
Shugaba kungiyar a jihar Komred Samson Almuru, ya shedawa taron manema labarai a Yola fadar jihar cewa kungiyar ba ta anfana ko da sau guda ba daga tallafin da gwamnati tarayya ke rabawa jihohi.
Ya ce abin takaici shine duk da kasawar da gwamnati ta yi na ware mata wani kaso na kudin Faris kulob Naira miliyan tara da ta karba daga gwamnatin tarayya bara don rage bashin da ‘ya’yan kungiyar ke bin ta.’ko Naira biliyan daya da gwamna Muhammadu Umaru Jibirilla ya sanar ya ware don rage bashin hakkokin da tsoffin ma’aikatan ke bi makonni uku da suka gabata, har yanzu ba su gani a kasa ba’ inji Komred Samson Almuru.
Wadannan kalamai na shugaban kungiyar tsoffin ma’aikata ta kasa reshen jihar Adamawa ya tada hankalin mukarraban gwamna Jibirilla dalilin da ya sa kwamishinan kudi na jihar Alh, Sali Yunusa ya kira taron ‘yan jarida don ya baiwa tsoffin ma’aikata hakuri da alkawarin zasu biya hakkokinsu da zaran kudin Faris Kulob da shugaba Buhari ya alkawarta sun samu.
Kawo yanzu, akwai tsoffin ma’aikata da suka share sama da shekara shida suna yi wa kudaden sallamarsu jiran gawon shanu a jihar Adamawa.

@isyakuweb--ku biyo  mu a Facebook
 
 

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN