Kwallon kafa- Issa Hayatou Ya Sha Kaye a zaben CAF


Labari da muka samu yanzu-yanzu ya nuna cewa Issa Hayatou ya sha kaye a zaben da aka yi na shugabancin hukumar kwallon kafa na kasashen Africa CAF.Ya sha kaye a hannun Ahmad Ahmad dan asalin kasar Madagascar inda Issa Hayatou ya tashi da kuri'u 20 shi kuma Ahmad Ahmad ya tashi da kuru'u 34.

Wannan lamarin ya kawo karshen shugabanci na shekara 29 da Mr Hayatou ya share akan karagar shugabancin.Tabbatattun labarai sun shaida cewa daga cikin kasashen da suka goyi bayan zaben Mr.Hayatou ya ci gaba da shugabancin CAF har da Najeriya.

Isyaku Garba   @isyakuweb .Ku biyo mu a Facebook https://web.facebook.com/isyakuweb 

AIKO DA LABARI

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN