Kebbi,Kakakin Majalisar dokoki ya yanke jiki ya fadi

Jaridar nigerianeye ta wallafa wani labari a shafin ta na yanar gizo cewa shugaban Majalisan dokoki na jihar Kebbi Hon. Samaila Abdulmumin ya yanke jiki ya fadi ranar Laraba 2/3/2017 da yamma a yayin da suke cikin duba wata kwangilar aikin hanya a garin Ribah da ke karamar hukumar Zuru ta jihar Kebbi.

Gwamna Atiku Bagudu ya gaiyaci Kakakin Majalisar dokoki na jihar Kebbi ne domin ya kasance a cikin tawagar sa zuwa wajen duba aikin.Jaridar ta kara da cewa bayan aukuwan lamarin,wasu jami'an tsaro sun garzaya da Kakakin zuwa Birnin kebbi a cikin wata motar daukan marasa lafiya da ba'a yi mata wani shaida ba.

A cewar jaridar,har ya zuwa lokacin da aka buga rahotun,ba a san takamammen rashin lafiyar da ke damun Kakakin Majalisan ba.Kuma kokarin da suka yi domin su sami bayani a takwarorin sa 'yan Majalisan dokoki na jihar Kebbi ya ci tura domin babu wanda yace da su uffan.

Isyaku Garba - Birnin kebbi
@isyakuweb  Ku biyo mu a Facebook

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN