A ‘yan shekarun baya da suka wuce musamman daga 2012 zuwa 2013 aka dinga samun
sakonnin musamman a shafukan sada zumunta na whatsapp,twitter da facebook kai
harma da sakonni na sms wanda a cikin sakonnin ana bukatar wai mutane su ziyyarci
bankin musulunci ta Jaiz su buda asusun
ajiya domin a ceci bankin ta Jaiz daga barazanar durkushewa wanda take fuskanta
saboda rashin kostoma masu hulda da bankin.
Wannan irin sakonnin sun sake bullowa kuma a whatsapp da
kuma facebook,dauke da sakon cewa bankin Jaiz tana kan hanyar durkushewa saboda
rashin kostoma masu buda asusun ajiya a bankin.A bisa wannan tubalin ne
ISYAKU.COM ta bi diddigi domin ta gano gaskiyar ko me ke faruwa ne akan wannan
zancen da yake yawatawa a shafukan sada zumunta game da bankin musulunci ta Jaiz.
A yayin da muka tuntubi babban ofishin bankin Jaiz ta kasa
game da wannan batun,wata wakiliyar bankin wanda bata son a fadi sunanta ta
tabbatar mana da cewa duk wadannan sakonnin da ke zagayawa game da bankin ba
gaskiya bane kuma ba bankin ne ya aika wannan sakonnin ba.Ta kuma kara da cewa
tuni bankin ta Jaiz ta nisanta kanta daga wannan sakonnin,jami’ar ta ce suna
samun karuwar sababbin masu buda asusun ajiya a bankin da kuma hulda da bankin Jaiz
a ko da yaushe saboda haka ba gaskiya bane cewa bankin na fuskantar barazanar
durkushewa saboda rashin masu hulda da bankin.
A ziyarar gani wa ido da ISYAKU.COM ta kai a reshen bankin
na Jaiz da ke garin Birnin Kebbi,mun gani ana hada-hada da jama’a kamar yadda
kowane banki na zamani ke yi,kowane ma’aikaci yana kan aikinsa haka kuma jami’an
tsaro na bankin suna kan aiki kamar yadda kowane banki ke gudanar da ayyukan ta
a kasarnan.
Isyaku Garba
@isyakuweb Ku biyo mu
a Facebook