Gwamna Atiku ya ba da Kwangilar yin Hanyoyi a Masarautar Zuru

Mai girma Gwamnan jihar Kebbi Sanata Atiku Bagudu ya ba da kwangilar aikin titi a Masarautar Zuru,ayyukan da ya kaddamar da fara aikin su ya hada da hanyar Riba zuwa Maga,Riba zuwa Wasagu  har zuwa Bena,haka kuma hanyar da ta taso daga garin Dabai zuwa Amanawa ta cikin garin Zuru.Gwamna Atiku ya ce wannan wani mataki ne na fara cika alkawari da ya yi a lokacin yakin neman zabe.

Gwamnan ya kuma ce Gwamnatin sa tana kokari akan ganin cewa Masarautar Zuru ta wadata da wutan Lantarki.Ya ce a yanzu haka an cire Bagudo, Ka'oje da Koko-Besse daga layin wutan Lantarki na Yelwa Yauri domin a inganta wutar lantarki ta Zuru.Majiyar mu ta ce haka zalika Gwamnatin Atiku Bagudu ta bayar da kwangilar gyara itatuwa da wayan mutan lantarki da ta dauko wutar daga Yauri zuwa Zuru.

Isyaku Garba
@isyakuweb  Ku biyo mu a Facebook

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN