Dalibai Inyamirai sun yi mubaya'a ga kasancewar Najeriya kasa daya





A yau dinnan dubu dubatan dalibai 'yan asalin kabilar inyamirai (Igbo) karkashin sahen dalibai na kungiyar Inyamirai na ohanaze ndi igbo suka aiwatar da zanga zangar lumana domin su nuna mubaya'ar su ga kasancewa Najeriya kasa daya su kuma tabbatar wa gwamnatin Najeriya goyon baya.Daliban sun zagaya titunan birnin Abuja har izuwa fadar shugaban kasa ta dutsen Aso.


A yayin da yake wa masu zanga zangan jawabi a dandalin hadin kai na kasa a Abuja, shugaban sashen dalibai na kungiyar Inyamirai ta ohanaze ndi igbo comared  Osisioma Osikenyi Igwe yace "al'umman Inyamirai sun yi mummunar kuskure a can baya,a yanzu kuwa basa son su sake maimaita irin wannan kuskuren"

Ya kuma bukaci al'umman kudancin Najeriya masu tada kayan baya da cewa su rungumi zaman lafiya,ya kuma roki gafara ga jam'iyyar APC da kuma gwamnatin Buhari saboda barazana da kungiyoyin Inyamirai masu tada kayan baya kamar IPOB da MOSSOB suka yi.

@isyakuweb - Ku biya mu a Facebook
http://web.facebook.com/isyakuweb

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN