An fara taron karawa juna ilimi mai taken "gina kasa ta hanyar dogaro da kai" a Birnin kebbi


A yanzu haka an fara gudanar da taron karawa juna ilini na lakca wanda hadaddiyar kungiyar Limamai da Malamai ta jihar Kebbi karkashin jagorancin Alh.Ibrahim Bayawa suka shirya wanda ake gudanarwa yanzu haka a dakin taro na sansanin Alhazai da ke hannun riga da Asibitin tarayya (Federal medical center) a garin Birnin kebbi.

Taron lakcan wanda ake sa ran za'a kammala shi a gobe yana dauke da taken "gina kasa ta hanyar dogaro da kai" kuma tuni masana akan bangarorin ilimi da rayuwa suka fara gabatar da jawabai na lakca ga mahalarta taron.

@isyakuweb - Ku biyo mu a Facebook
https://web.facebook.com/isyakuweb

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN