Dan shekara 23 ya auri Mahaifiyar sa

Mazauna wani kauye a kasar Zambia sun wayi gari cikin ganin wani abin al'ajabi a yayin da wata Mata mai shekara 40 ta bukaci Kotun garin ta daura mata aure da dan da ta haifa mai shekaru 23.Matar dai Madam Mbereko ta bukaci a daura masu aure ne da dan nata Farai Mbereko a cewar ta domin sun tsunduma cikin soyayya shekaru uku da suka wuce.

Rahotanni sun nuna cewa Alkalin Kotun garin bai aminta da wannan auren ba,a sanadin haka ma'auratan suka je wani gari aka daura masu aure.A nata bayanin,Uwar sabon mijin nata kuma dan ta Farai,cewa ta yi bayan rasuwar uban shi dan nata Farai,ta sha matukar wahala wajen biya masa kudin makaranta har izuwa wannan lokaci da Allah ya sa ya zama abin da ya zama a yanzu,"babu wanda ya taimaka min wajen shan wahala da shi kuma ba zan bari haka kawai wata mace ta more shi ba daga sama" in ji Mbereko uwar mijin ta.

Wani dattijo mazauni wannan kauyen cewa yayi "idan a lokacin da ne,ita Uwar da Dan nata za'a kashe su ne a bisa al'ada domin hakan yakan janyo bala'i a kauyen.Amma da yake muna cikin wani zamani na tsoron 'yan sanda ya zama wajibi mu yi korafi kawai".Wannan Matar dai a yanzu haka tana dauke da cikin sabon Mijin nata kuma Dan ta na cikin ta.To jama'a...wannan Da ne kenan ake shirin haifawa ko Jika ?


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN