Aisha,Macen da ke farautar 'yan Boko Haram


Wani labari da naij.com ta ruwaito ya nuna cewa Aisha  Bakari Gombi wata Mace ce mai farautar 'yan kungiyar boko haram, jaruntar wannan Macen ya sa ana kiran ta "Sarauniyar Mafarauta".Aisha haifaffar kauyen Duggu ce wanda tafiyar minti 30 ne daga kauyen Chibok,inda 'yan boko haram suka sace 'yan Makarantar  mata shekarar 2014.
Aikwai dubban Masu farauta da Hukumar Sojin Najeriya ta dauka aikin sintirin wucin gadi,amma Aisha tana daya daga cikin Mata kalilan da sukace jajirce da wannan sintirin farautar 'yan kungiyar boko haram din.Duk da yake Aisha Musulma ce amma ita da sauran masu farautar sukan yi amfani da wasu tsari na gargajiya domin kare kan su daga albarush i kafin su tsunduma a cikin daji.Asha 'yar shekara 38,tana jagorantar runduna ce ta Mafarauta 'yan tsakanin shekaru 15-30 kuma sukan yi magana ne ta hanyar amfani da sauti irin na dabbobi ko tsuntsaye.

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN