Daya daga cikin jaruman da finafinan Hausa da taurararonsu ke haskawa Zaharaddeen Sani, ya musanta zargin da ake yi masa da neman maza.
A hirarsa da jaridar Premium
Times mai yada labarai a yanar gizo a ranar Lahadi 28 ga watan Janairu
shekarar 2017, matashin dan asalin Jihar Kaduna ya bayyana wannan zargin
da cewa, zuki tamalle ne da kuma neman bata masa suna.
A
hirar, jarumin finafinan ya bayyana cewa, yana da mata da 'ya 'ya biyu
Maryam da Mannuira, ya sannan ya kuma bayyana aniyarsa na karin wani
auren da wata jaruma a Kannywood wacce ya dade yana so, sai dai har yanzu ba ta amince ba.
Ya kuma ci
gaba da bayyana alkarsa da sauran jarumai maza da mata irinsu Ali Nuhu
da Jamila Umar da sauransu da cewa kyakkyawa ne.
Jarumin
ya bayyana matakin korar da kungiyar masu shirya finafinai ta MOPPAN ta
yiwa Rahma Sadau da cewa ya yi daidai, sannan kuma ya ce idan za a
rinka yanke hukunci na ba sani ba sabo ga wanda ya karya doka to za a
gyara sana'ar.
Baya ga sana'ar fitowa a finafinai a cewarsa, ya na sana'ar sayar da motoci domin shi ma'abocin motocin kawa ne.
An
dai sha zargin fitattun jarumai masu shirya finafinai da badala a ciki
da wajen sana'arsu ta shirin fim, hakan ya sa suka sa wando daya da
Hukumar tace finafinai da dab'i ta jihar Kano musamman a lokacin mulkin
Ibrahim Shekarau.
Har ta kai a
shekarar 2016 Adam A. Zango ya rantse da Al kur'ani tare da dora shi a
kansa a cikin wani shirin talbijin a yayin hira da shi, don ya wanke
kansa daga zargin neman maza.
NAIJ.COM HAUSA
Tags:
LABARI