Hedikwatan Birnin kebbi sun wayi gari da taro wanda ya dauki hankali,koda
suka bincika 'yan Darikar Tijaniyya ne suka fito cikin daruruwan su
domin nuna murna da haihuwar Mazon Rahma watau Annabi Muhammadu
sallalahu alaihi wasalam.Masu zagayawan sun kunshi matan aure, budare. da kuma yara.Zagayen na awa uku ya samu halartar manyan Shehunnan darikar Tijjaniyya.
Daga bisani aka fara raye-raye domin nuna murna.Duk zawiyyon dake cikin birnin Jaha sun halarci taron.Daga karshe khalifan Ahmad Usman Muktar ya gaya wa manema labarai cewa suna maulidin ne akan hujja ba.a jahilce ba, Khalifan ya kara da cewa Annabi ne yace suyi Mauludi domin nuna soyya a agare shi da iyalan gidan sa.Shugaban ya mika godiyar sa ga mabiya Darikar inda yayi kira ga jama'a da su so Annabi da gaskiya.Daga karshe ya gode ma gwamnatin jaha domin kaso da ta bayar lokacin bukukuwan.
Tags:
LABARI