GWAMNATIN SOKOTO TA DAKATAR DA HUKUMAR HIZBAH.


Gwamnatin jihar Sakkwato karkashin jagorancin Gwamna Aminu Waziri Tambuwal ta dakatar dahukumar Hizba daga zartar da duk wani hukunci a Sokoto da kewaye.
Kwamishinan lamurran Addini Mani Mai Shinko Katami ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ta fita daga ofishinsa a yammacin jiya Asabar. Tare da bukatar Hukumar ta Hizbar su mika duk wani abu na gwamnati da yake hannunsu.
Har yanzu dai gwamnatin jihar ta Sokoto ba ta fadi dalilin dakatarwar ba. Amma wasu na ganin wannan dakatarwar nada nasaba da bayanin da hukumar ta Hizba ta fitar game da bikin 'yar Gwamna Tambuwal wanda aka yi a kwanakkin baya, inda rahotanni sun nuna cewa hukumar ta kama wanda ya hada kayan kidan a wurin shagalin bikin.
RARIYA

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN