AN TSINCI JARIRI A WANI KANGO A GARIN AMBURSA A JIHAR KEBBI

An Tsinci Jariri A Wani Kango A Garin Ambursa Ta Jihar Kebbi
Hukumar Hisba ta jihar Kebbi na bada sanarwar an kawo mata wani yaro jariri sabon haihuwa wanda aka ajiye a cikin wani kangon gida a garin Ambursa dake karamar hukumar mulki ta Birnin Kebbi.
An tsinci jaririn ne cikin buhu, yana kuka, a ranar Juma'ar da ta gabata da misalin karfe 2:30 yamma.
Hukumar na kira ga jama'ar yankin na Ambursa da duk wanda ya san uwar wannan yaro ko kuma wata da ake tuhuma da nata ne da a sanar da hukuma don daukar matakin da ya dace.
Sanarwar na dauke da sa hannun mataimakin shugaban Hisba na jihar Kebbi, Alhaji Mamuda Geza
RARIYA

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN