Yansandan a
jihar Kaduna da ke a Arewacin Najeriya sun sanar da cafke ‘yan fashi
sama da 400 wadanda ake zargi da laifin yin garkuwa da mutane da kuma
satar shanu a cikin shekarar 2016.
Kwamishina
‘yansandan jihar, Mista Agyelo Abeh ne ya tabbatar da kama mutanen ya
kuma shaida cewa sun kwato muggan makamai sama da 100 daga hannu ‘yan
fashin.
Mista Agyelo ya ce tuni aka mika 384 daga cikin wadanda aka kama gaban kuliya, yayin da ake ci gaba da binciken sauran.
Matsalar satar shanu da kuma yin garkuwa da mutane ya zama ruwan dare gama gari a Najeriya a shekarun baya bayan nan.
RFI Hausa
Mista Agyelo ya ce tuni aka mika 384 daga cikin wadanda aka kama gaban kuliya, yayin da ake ci gaba da binciken sauran.
Matsalar satar shanu da kuma yin garkuwa da mutane ya zama ruwan dare gama gari a Najeriya a shekarun baya bayan nan.
RFI Hausa
Tags:
LABARI