ZA MU MAYAR DA SAMBISA WURIN ATISAYEN MU- SOJAN NAJERIYA

Hukumomin soji a Nigeria sun ce za su mayar da dajin Sambisa - inda ya kasance sansanin mayakan Boko Haram tun shekara ta 2013 - wurin atisaye.
A makon jiya ne dai shugaban kasar, Muhammadu Buhari, ya tabbatar da cewa sojojin sun yi nasarar kwace dajin daga hannun mayakan.
Mai magana da yawun rundunar sojin kasa Birgediya-Janar Sani Usman Kukasheka ya shaida wa BBC cewa za a yi hakan ne domin tabbatar da cewa ''wasu miyagun mutane ba su fake a wannan dajin ba.''
Janar Kukasheka ya ce kuma nan gaba kadan za su yi wa 'yan kasar bayanin abubuwan suka tarar a dajin bayan fattatakar mayakan Boko Haram daga sansanoninsu.
BBC HAUSA

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN