Shugaban
rundunar sojin Najeriya laftanar Janar Tukur Buratai, ya bukaci sojojin
dake fafatawa da ‘yan Boko Haram a yankin Arewa maso gabas da suyi
shirin fadan karshe da’ yan ta’addan,
domin kuwa babu tsarin shiga Sabuwar shekarar 2017 ba tare da an gama da su ba.
domin kuwa babu tsarin shiga Sabuwar shekarar 2017 ba tare da an gama da su ba.
“Kodai
mu samu nasarar karkade kurarsu da ta rage ko kuma mu cigaba da
fafatawa ba kakkautawa, a cikin wannan halin kangin maras dadi na
ta’addanci a yankin nan na Arewa maso gabas”.
“yana
mai fada da kakkausar murya ga rundunar sojojin, tare kuma da jaddada
cewa watan Disamba (December) yadda yazo a watan karshe na shekara haka
su ma ‘yan Boko Haram kasrshensu ya gabato”
Buratai
yayi alkawarin mayar da sojojin barikinsu a cikin shekarar da zamu
shiga ta 2017. Janaral Buratai yayi alkawarin zuwa da kansa filin daga
yayin da ake fafatawa da’ yan Boko Haram din.
Yadai yabawa sojojin tare da nuna jin dadinsa a kan irin sadaukar da suke yi na kare kasarsu.
A
karshe kuma yayi kara ga duk jagororin bataliyoyin sojojin da su shirya
kai hare-hare zafafa aka ‘yan Boko Haram din musamman sojojin sama.
Daga Labarai24.
Tags:
LABARI