Akwai tashin hankali a jihar Kaduna,yayinda matasan addinin kirista sun sha alwashin zasu kai kari duk lokacin da Fulani makiyaya suka sake kawo musu hari a kudancin jihar Kaduna.
Jaridar Punch ta bada rahoton cewa Matasan suna wannan barazanar ne bayan sun gano wani munafurci a bangaren jami’an tsaro.
Kana sunyi kiraga majalisar dokokin jihar Kaduna su tsige Gwamna El-Rufai da gaggawa saboda laifin hada baki da yan taádda su kasha yan Najeriya.
Shugaban Matasan yace: “Ko Fulanin yan Najeriya ko yan kasan waje ne, mu matasan Kirista mun yi ittifakin cewa wannan yunkurin kasha kiristoci ne a Najeriya. Saboda haka, muna kira ga Kirista su dau makami.”
Mudathir Ishaq naij.com
Tags:
LABARI