1. Ka ajiye wayarka yayin da Iyayenka suke yi maka magana. Kar ya zamanto suna yi maka magana, kai kuma kana danne-danne awayarka. (Browsing ko Chatting). Wannan Rainin wayo kenan.
2. Ka rika neman shawara a wajensu. Kuma
idan sun baka shawara ka rika dauka kana amfani da ita. Koda a kan neman
aurenka ne- Girmamawa kenan.
3. Kar ka rika tsoma baki acikin
maganarsu, har sai idan sunyi maka izini. Kuma duk zancen da zakayi
dasu, wajibi ne kayi amfani da zababbun kalmomi na Musamman.
4. Koda an samu rashin fahimtar Juna a
tsakaninka dasu, kar ka yarda su fahimci ranka ya baci, ballantana har
ka furta musu wata mummunar kalma wacce zata Sosa musu rai.
5. Ka rika yaba musu a bisa dukkan abinda
su kayi maka komai kankantarsa. Koda addu’a sukayi maka, to lallai ka
tsaya kayi musu godiya a bisa wannan.
6. Ka rika girmama ‘Yan uwansu da
abokansu. Ka rika ziyartarsu kana Kyautata alakarka dasu. Domin
girmamasu kamar girmama Mahaifan naka ne.
7. Duk lokacin da wani abin farin ciki ya
sameka, To ka fara gaya ma Mahaifanka kafin ka gaya ma kowa. Amma idan
abin bakin ciki ne, Kar ka yarda suji abinda hankalinsu zai tashi.
8. Kar ka manta da Muhimman Gudunmuwar da
Iyayenka suka bama rayuwarka. Ka rika ji a cikin ranka cewar babu
abinda zaka yi ka iya biyansu.
9. Wani lokacin zasu gaya maka labari
kuma washegari su sake maimaita maka, sun manta cewa sun riga sun gaya
maka. To amma duk da haka kar ka nuna musu kosawarka wajen sauraronsu.
10. Abinda ya wuce ya riga ya wuce. Kar
ka rika zargin iyayenka ko tuhumarsu da wani laifi. Kuma kar ka rika
tuno musu wani mummunan labari.
11. Kar ka rika shiga gaban Mahaifinka
idan zaka yi tafiya. Kuma duk lokacin da kake zaune tare da shi a gida
ko a Mota, Ka zauna cikin ladabi. Ka tashi tare da ladabi.
12. Ka guji zagi ko bugun kannenka Ko Jikokin gidanku akan kananan abubuwa. Watakil yin hakan zai sosa zuciyar Mahaifanka.
13. Ka rika amfani da Murya mai taushi,
lafazi mai taushi, Kallo mai taushi a duk lokacin da kake tare da
Mahaifanka. Kuma kar ka daga muryarka sama da tasu.
14. Ka kiyaye Sirrin mahaifanka. Kar ka rika daukar labarin da zai janyo zubewar Mutuncinsu kana fadawa wa mutane.
15. Mahaifanka sune abu mafi daraja, mafi
tsada wanda ka mallaka. Don haka ka lailayesu, ka kula dasu fiye da
yadda kake kulawa da kanka.
16. In dai kana da hali, kar ka yarda
kaci wani abu mai dadi ba tare da ka saya musu irinsa ko fiye dashi ba.
Kar ka yarda kasha wani abu mai sanyi mai dadi wanda su basu sha irinsa
ba.
17. Ka kyautata musu suturar da suke
sanyawa. Da kuma wajen kwanansu da abincinsu. Ka tabbatar ka ingantashi
fiye da naka na kanka.
18. Duk lokacin da basu da lafiya, Kar ka
wakilta wani ya kula dasu. A’a kai ne zaka kula dasu. Ka kyale duk
harkokinka. Kar ka manta lokacin da kayi zazzabi sanda kana yaro, ai ba
su wakilta maka kowa ba. Su suka kula dakai.
19. Kar ka rika jiran wai sai sun rokeka abu sannan kayi musu, a’a ka tabbatar kana yi musu tun kafin su nema.
20. Idan kana zaune gida guda ko gari
guda tare dasu, Kar ka yarda Safiya ta wuce baka je ka gaida su ba. Idan
kuma kana aiki a wani garin ne, to koda duk Karshen mako ne, Sai kaje
ka duba su Kuma ka nemi afuwarsu bisa rashin ganinka da ba su yi ba.
21. Ka kasance ko yaushe cikin yin addu’a
agaresu, ba wai sai a gurbin Sallah ba. Kuma ka rika neman afuwarsu da
zarar ka fahimci wani abu ya sosa musu rai. Koda ba kai ne ka aikata ba.
22. Idan kuma sun rasu, to kar ka dena addu’a a garesu har karshen rayuwarka. Kuma ka rungumi zumuncinsu ya zama naka.
23. Ka rika shiga sha’anin kannenka da
yayyenka gwargwadon yadda zaka kyautata alakarka da su. Kar ka rika nuna
‘Yan Ubanci ga wasu daga cikin kannenka. Yin hakan zai sosa zuciyar
mahaifinka.
24. Ka rika kiran mahaifanka da sunaye na
girmamawa. Kar ka rika kiransu da sunayensu. Watakil yin hakan zai
zubar da mutuncinsu a gaban mutane.
25. Idan sun samu rashin fahimtar Juna a
tsakanin junansu, Kayi kokari ka daidaita su ba tare da ka goyi bayan
kowanne daga cikinsu ba.
26. Ka kiyaye kar ka yarda ka fifita matarka akan iyayenka. Ana chanjin Mace, amma ba’a chanza iyaye.
Ya Alah ka jikan Iyayenmu ka gafarta
musu. Ka kyautata makwancinsu ka haskaka Kaburburansu. Kayi musu rahama
kamar yadda suka ji kanmu tun muna kanana.
Daga ZAUREN FIQHU
Tags:
FADAKARWA