Wani na Hannun Damarsa ya sanar damu kamar haka "A ranar Asabar 4 ga Watan Yuni na wannan Shekaran 2016 ne Gidan Talabijin na DITV dake Jahar Kaduna Zasuyi Hira da mai Gidan mu Adam A Zango wanda Masoyansa da dama sun dade basuji duriyarsa ba a Kafafen Yada Labarai, sai kwatsam wani mai gabatar da shirin Mushakata a Gidan Talabijin din wato Gabiya ya kira Adam Zango a cikin shirin sannan yayi Alkawarin zuwa Yau din, amman kaga bai samu zuwa ba saboda yar Gajeruwa Rashin Lafiya dayi fama dashi" kaga tsabar rashin samun hutu ne ke kawo hakan, a gaskiya ni wani lokacin wallahi har tausayi yake bani don irin aikatuwar da yake yi, sannan kaga kuma wani dadin da dawar da zai baka tausayi yadda sauran yan fim zasu fito su sakata su wala shi baya iyawa domin duk inda ya bi Jama'a basu barinshi amman kasan kaunace ta kawo hakan, to kaga sai dai daga gida sai ofis dinsa ko gun aiki.
Da muka leka dan kai tamu ziyarar da mai fatan kara samum lafiya dan gane da rashin lafiyar da kafan Talabijin din DITV tayi na baida lafiya an kara mai Ruwa, bayan jajanta mai da mai fatan Alheri, sai ya baiyana mana ciwon tapot ne ya dan kwantar dashi amman yanzu Alhamdulillah ya samu sauki, sannan kuma yayi Godiya ga Masoyansa da Addu'o'i dasuke masa wanda yake matukar bukata daga garesu yana Godiya matuka, dafatan Allah yabar zumunci.
(Daga Kannywoodtoday)
Tags:
LABARI