BOKO HARAM TA SAKE KASHE WANI BABBAN SOJAN NAJERIYA

Rahotanni sun nuna cewa Boko haram ta sake kashe wani babban sojin Najeriya Laftana kanar mai kula
da bataliya ta 114 ta dakarun musamman ya hadu da ajalin sa ne yayin wani kwanton bauna da 'yan boko haram din suka yi ranar Litinin 14/11/2016 da safe inda suka  halaka shi tsakanin Bita da Piridang.

Jaridar Premium times ta ruwaito cewa,motar da kwamandan ke ciki ne ya taka wata nakiya da aka bi
nne a gefen titi,bayan fashewar nakiyar kwamandan bai raunata ba amma lokacin da ya fito daga motar don ya duba barnar da nakiyar tayi sai 'yan boko haram din suka buda masa wuta da bindigogi.

Sojojin dai ance suna kan hanyar su ce ta zuwa Yola ta jihar Adamawa daga Bita ta jihar Barno,hukumar sojin Najeriya dai ta bakin kakakin ta, ta ce bata da masaniya game da wannan al'amari ko mutuwar laftana kanar Umar.

(Daga naij.com)

Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN