SOYAYYAR ADAM ZANGO DA ZAHRA BUHARI

 
 A yan kwanakin nan wata jitajita kan shahararran Mawaki kuma Jarumi Adam A. Zango da diyar shugaban Kasan Najeriya Zahra Buhari ke yaduwa a shafin yanar gizo na sada zumunta ke ta bazuwa akan soyayya na tsakaninsu, ganin wani hoto da jarumin yasa a shafinsa na sada zumuntar facebook da Instagram wanda suke tare da 'yar shugaban Kasa Muhammad Buhari yasa wasu keta baza jita jiar cewa suna soyayyane.

Dan ganin hakan yasa wakilinmu a Jahar Kaduna baiyi wata wata ba inda ya nemi jarumin ta wayarsa inda bai sameshiba sai yayi tattaki zuwa ofishinsa dake Dandalin Murtala Square a Kaduna, da zuwansa kuwa yayi arba da Jarumin sannan ya tambayeshi shin ko ya gaskiyar batun soyayyarsa da diyar shugaban Kasa Muhammad Buhari Zahra, sai yace " Uhmm abin sirri ne" sai kuma yayi gum bai kara cewa komai da wakilin namu ya kara matsala lamba akan wasu zasu so sanin sirrin dake tattatare da batun sai yace "Magana ta tafarko dai itace Abin sirri ne". To me zakace ga masoyanka "Ina masu fatan Alheri sannan a ranan Juma'ar nan zan sako masu fim din Ramlah wanda nasan suna nan suna jiranshi".

Tun dai ranan Talatar nan ne da jarumin ya sanya hotonsa da Zahra Buhari wannan Jita jitar ya bazu.
Labari daga kannywoodtoday.


Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN