RAHAMA SADAU TA DIRA AMERICA

Shararriyar jarumar fina-finan Hausa Rahama Sadau daga Najeriya ta isa kasar Amerika domin gudanar da aikin hadinguiwa da fitacxen mawakin nan na Amerika Akon da kuma Shahararren Ma shiryin shirya fina-finan dan asalin Najeriya Jeta Amata suka gayyace ta bayan koran da hadakar Kungiyar masu shirya fina-finan Hausa MOPPAN sukayi mata a farkon wananna watan.

MOPPAN kungiyace dake ladaftar da duk wani wanda yayi ba dai dai ba daga dukkannin kungiyoyin gamayyar fina-finai da wakoki, adan haka ne wannan kungiya ta dauki matakin dakatar da ita a cewar kungiyar an sameta laifuffuka sau hudu.

Bayan dakatar da ita ne fitaccen mawakin Turanci na Kasar Amuruka Akon wanda dan asali Kasar Senegal ne dashi da fitaccen Maishirya fina-finai Jeta Amata wanda dan Kasar Najeriya inda suka gayyaci Rahama Sadau domin yin aiki tara a shafukansu na twitter.

Dan gane da wannan gayyata ne Babban Malamin Addinin Musuluncin nan Malam Aminu Daurawa dake Jahar Kano a Najeriya inda ya ja hankalin jarumar da karta amshi gayyatar zuwa da mafi dacewa da ita shine tayi aure domin haka Addinin musulunci ya tanadar a matsayinta na Musulma

Yanzu dai haka Rahama Sadau na Los Angeles wanda zasu fara aikin fim din Jeta Amata mai suna "The American King."
(Daga Kannywoodtoday)

HOTUNAN RAHAMA SADAU A KASAR AMURUKA KENAN.





Post a Comment

RUBUTA SHARHI KO RA'AYINKA KAN WANNAN LABARI

Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN